An yi wani rubutu dake nuna wariyar launin fata a jikin kofar gidan dan wasan kasar Suwidin Ibrahimovic. Al'marin ya faru ne dai bayan dan wasan ya bayyana cewa ya sayi kaso daga kulob din kwallon kafa na Hammarby. Kamar haka ne dai aka rubuta kalmar "Yahuda" a gaban gidansa inda kalmar ta kasance sunan mutumin ya ci amanar annabi Isa. Shugaban Ofishin 'Yan Sanda na birnin Sitokuhom Bengt Dahnell ya bayyana cewa suna iya kokarinsu wajen ganin sun kama wanda ya yi rubutun. A gefe guda an kara yin wani rubutu dake nuna wariyar launin fata jikin mutum-mutumin Ibrahimovic dake birnin Malmo inda rubutun ya yi wa dan kwallon barazanar kisa sannan ya bayyana cewa shi ba dan kasar ba ne, asalin sa ya zo ne daga cikin mutanen "Gispy".
No comments:
Post a Comment