Tsohon Dan wasan kungiyar Barcelona Samuel Eto’o yayi ritaya daga buga wasan kwallon kafa. Kanfanin Dillancin Labarai na Najeriya ya bayyana cewa, Samuel Eto’o Dan shekaru 38, ya ajiye Takalmi ne bayan shafe shekaru 22 yana buga wasa. Shi ne Dan wasan da yayi fice a cikin ‘yan wasan da suka fito daga nashiyar Afirka. Ya dai cira kofinan Laliga guda hudu da kuma kofin zakarun Turai na champion guda Biyu, a kingiyar ta Barcelona.
No comments:
Post a Comment